Buhari ya kafa kwamitin rage talauci a Nigeria

Date:

Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya kaddamar da kwamiti na musamman don rage talauci a tsakanin yan kasar da kuma bijiro da dabarun bunkasa tattalin arziki.

A cikin rahotonsa na baya-bayan nan, Bankin Duniya ya ce hauhawar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya na kara talaucin da kuma tabarbarewar harkokin kasuwanci.

Bankin ya ce kimanin ‘yan Najeriya miliyan 7 ne suka fada cikin talauci a shekarar 2020 saboda tashin farashin kawai.

A wata sanarwa da Femi Adesina, mai magana da yawun shugaban, ya fitar a ranar Talata, an bayyana mataimakin Shugaban kasa Yemi Osinbajo ne zai jagoranci kwamitin.

BBC Hausa ta rawaito Buhari ya sake nanata alkawarinsa na fitar da ‘yan Najeriya miliyan 100 daga kangin talauci cikin shekaru goma, tare da kyakkyawan tsarin bincike don aiwatarwa da kuma samar da kudade.

85 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...