An Gurfanar da Wata Mata da ake Zargi da Kashe Kishiyar ta a Kotu

Date:

Daga Nusaiba Aliyu Salga

Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Kano a ranar Alhamis ta gurfanar da wata mai suna Fadima Dahiru mazauniyar Unguwar Farawa da ke karamar Hukumar Kumbotso a gaban kotu a kan zargin kashe kishiyar ta Mai Suna Waseela har lahira.
 Da take gurfanar da wacce ake kara a gaban Mai Shari’a Zuwaira Yusuf, Lauya mai shigar da kara Barista Khadija Umar daga Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Kano ta yi zargin cewa Fadima Dahiru a ranar 6 ga Mayu, 2019 da misalin karfe 15:30Hrs ta yi amfani da abu mai kaifi tare da raunata Waseela Wanda hakan yayi sanadiyyar mutuwarta har lahira nan take.


 “Kin aikata wani laifi wanda yake karkashin hurumin wannan Kotun mai alfarma da Wanda ya haddasa kisa waseela”.


 Khadija Umar ya fadawa kotun cewa laifin da ake karar  Fatima a Kansa ya sabawa sashi na 221 (A) na pinal code.


 Lauyan da ke kare wadda ake tuhuma Barista Bashir Abdullahi Sufi ya roki kotun da ta ba da damar sauraren karar a rana mai zuwa, mai shari’a Zuwaira Yusuf ta karbi rokon kuma, ta dage sauraron karar zuwa 22 ga Yuli, 2021

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Hajjin bana: Za mu yi duk abun da ya dace don kyautata walwalar alhazan Jihar Kebbi – Amirul Hajji

Daga Ibrahim Sidi Muhammad Jega.   Shugaban kwamitin aikin hajin bana...

Bayan dawo da Gwadabe Anti daba, Yansanda sun kama yan daba 33 a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar Yansanda ta Kasa reshen jihar...

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...