Buhari Ya Sake Jaddada Kalaman Da Kamfanin Twitter Ya Goge

Date:

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya sake nanata matsayarsa da ya bayyana a baya, ta cewa zai yi maganin masu ta da kayar baya a kudu maso gabashin kasar “da irin yaren da suka fi fahimta.”

Buhari na nuni ne da irin tsauraran matakan da jami’an tsaron kasar ke shirin dauka akan mayakan kungiyar IPOB da ke fafutukar ballewa daga Najeriyar.

“Kamar yadda na fada a baya, za mu dauki mataki akansu daidai da irin yaren da suka fi fahimta.” Shugaban na Najeriya ya fada yayin wata hira ta musamman da ya yi da gidan talabijin na Arise TV a Legas.

Wadannan kalamai shugaban ya wallafa a shafin Twitter a makon da ya gabata, lamarin da ya sa kamfanin ya goge sakonsa.

A wani abu da ake ganin martani ne, hukumomin Najeriya sun haramta amfani da kafar.

“Mun ba ‘yan sanda da sojoji umarnin su dauki tsauraran matakai akansu, kuma ku tsaya ku gani, nan da wasu ‘yan makonni za ku ga canji.” Shugaban ya kara da cewa.

Buhari ya ce sun ba manyan hafsoshin tsaron kasar dama su zagaya sassan kasar don su ga yadda matsaloli tsaron suke.

“Za su tabbatar da cewa sun maido da zaman lafiya, ba ma so mu ta yayata shirin da muke yi ne, gudun kada mu ankarar da miyagu.”

Sai dai a wannan karon ya hada har da ‘yan bindiga da ke kai hare-hare a arewa maso yammaci.

Buhari ya kai ziyara jihar ta Legas ne a ranar Alhamis, inda ya je kaddamar da wasu ayyuka ciki har da bude tashar hanyar dogo da aka kammala wacce za ta rika tashi daga Legas zuwa Ibadan.

63 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da nuna tallan maganin Gargajiya a Fina-finai da yawo a tituna

A wani mataki na tabbatar da bin ka'idoji tare...

Da dumi-dumi: NNPP ta nemi afuwar Tinubu kan kalaman suka da ake zargin Kwankwaso ya yi masa

  Jam’iyyar NNPP ta nemi afuwar Shugaban kasa Bola Tinubu...

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...