Ganduje bashi da Hannu a Zanga-zangar da mukai a kaduna – Ayuba Wabba

Date:

Daga Safyan Dantala Jobawa

Kungiyar Kwadago ta Kasa ta Musanta zargin da Gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufa’i yayi na cewa Gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ne ya baiwa Kungiyar Kwadagon kudi domin su yi masa Zanga-zanga a kaduna.

Cikin Wata Sanarwa da Kadaura24 ta samu Mai dauke da sa Hannun Shugaban Kungiyar Kwadagon ta Kasa Comrade Ayuba Wabba, yace Ganduje bashi da Hannu ta kowacce fuska akan Zanga-zanga da muka gudanar.

Sanarwar tace Kungiyar ta gudanar da Zanga-zangar ne kawai Saboda yadda Gwamna Nasir El-Rufa’i yake cisgunawa Ma’aikata a jihar da Kuma yadda yake korarsu Daga aiki ba gaira Babu dalili.

“Mun ci Karo da Wani video da ya nuna Gwamna Nasir El-Rufa’i Yana zargin Ganduje da bamu kudi domin muyi Zanga-zanga,Ina so El-Rufa’i ya sani Kungiyar mu Bata yarda Wani ya shigo Cikinta har ya Bamu kudin don muyi Wani abu”. Inji Wabba

Sanarwa tayi Kira ga jama’an Tsaro da su Sanya idanu domin gudanar da aikin su yadda ya dace Saboda yadda El-Rufa’i yake yiwa Ma’aikatan da Kungiyar Kwadago baraza, Inda yace Barazanar sa bazata Hana Kungiyar neman Hakkin ‘ya’yanta ba.

Daga Karshe Ayuba Wabba a Cikin sanarwar yace Kungiyar su kowa ya santa da dattako da gudanar da aiyukanta akan tsare, yace zasu tabbatar sun ci gaba da kasancewa akan Wannan Matsayi domin Kare Martaba da Mutincin Ma’aikata a Kasar nan

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...