Kano Pillars ta dawo matsayi na daya a gasar 2020/2021NPFL

Date:

Zaharadeen saleh

Kungiyar kwallon kafa ta katsina united ta buga daya da daya da kungiyar kwallon kafa ta kano pillars, a cigaba da gasar cin kofin kwallon kafa ajin firimiya ta Nigeria a zagayen wasa mako na 22 da suka fafata a filin wasa na muhammad Dikko dake jihar Katsina, a lahadin nan.

Tunda farko kungiyar katsina utd ce ta samu bugun daga kai sai mai tsaran gida a mintina 24 da fara amma dan wasan ta Ahmed ya zubar.

An akai kimani minti 27 dan wasan kano pillars Rabi’u Ali ya samu nasarar jefawa kano pillars kwallo aragar katsina utd, an akai kimani mintina 34 dan katsina utd mai suna Abdulrashid Ahmed ya rama mata kwallon.

A yanzu bisa kunnen doki da kano pillars ta buga da katsina utd ta dawo matsayi na daya da maki 41 daga wasanin 22 data fafata a kakar wasa ta bana.

Ga sakamakon ragowar wasanin mako na 22 da aka buga ranar lahadin nan.

Plateau utd fc 4 v wikki Tourists 1

Nasarawa utd 3 v Heartland fc 1

Rivers utd fc 0 v Abia warriors fc 0

Jigawa G. Stars 1 v Dakkada fc 1

Fc Ifeanyi Uba 1 v Sunshine stars 0

MFM fc 1 v Lobi Stars fc 0

Adamawa utd 3 v Warri Wolves 3

A ranar Litinin 24 /05/2021 za’a kara tsakanin
Akwa utd fc v Enugu Ranggers fv

179 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...