Yajin Aiki: Gwamnatin Tarayya ta baiwa El-Rufa’i Umarni

Date:

Daga Muhd Kabir

Gwamnatin Tarayya ta ce ta zata Sanya Baki  kan yajin aikin da ke gudana a Kaduna biyo bayan barazanar da ma’aikata a bangaren wutar lantarki suka yi na jefa kasar baki daya cikin duhu.


 Ministan kwadago da samar da ayyuka, Sanata Chris Ngige ya bayyana hakan a wata sanarwa da Mista Charles Akpan, Mataimakin Daraktan yada labarai da hulda da jama’a a ma’aikatar ya sanya wa hannu a ranar Talata a Abuja.

 Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) da (TUC) sun fara yajin aikin gargadi na kwanaki biyar wanda suka fara a ranar Litinin kan korar ma’aikata 4000 da gwamnatin Kaduna ta yi.


 Ngige ya roki gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El ‘Rufai, shugaban NLC, Com. Ayuba Wabba da shugaban TUC, Mista Quadiri Olaleye da su hau teburin Sulhu domin sasantawa Kan lamarin.


  “Muna fata kuma muna kira ga gwamnan jihar Kaduna da kar ya kara dagula lamura zuwa irin matakin da ya zama ba za a iya shawo kansa ba.


 ”Muna kuma yin kira ga shugabannin cibiyoyin kwadagon da su sauka daga aikin domin samar da hanyar tattaunawa.


 “Ma’aikata ta na shiga cikin lamarin saboda haka ta yi kira ga bangarorin da ke fada da su ba da zaman lafiya dama,” in ji shi.


  Ministan ya kuma yi kira ga dukkan ma’aikata da aiyukansu suke da muhimman ayyuka Kamar likitoci da ma’aikatan jinya da kada su shiga yajin aikin.


 Ya kara da cewa, mafi mahimmanci, ina kira ga ma’aikata a bangarori masu muhimmanci da kar su taba kayan aikin lantarki ko na ruwa domin kar jefa mutanen jihar Kaduna da ma kasa baki daya wahalhalu.

65 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...