Hawan Nasarawa: Fulani Ku Dawo Kano da kiwo ko a daina tsangwamar ku- Ganduje

Date:

Daga Kamal Yusuf Daneji

Gwamnan jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya bukaci Fulani makiyaya Yan asalin jihar Kano wadanda suke gudanar da harkokin su na kiwo a kudancin Kasar nan dasu dawo Kano domin kaucewa tsangwamar da ake yi musu a Wasu shiyoyin Nigeria.

Gwamna Ganduje ya bayyana hakan ne Yayin daya karbi bakuncin Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero a Gidan Gwamnati Wanda zaje domin Taya Gwamnan Murnar Sallah Karama yayin Hawan Nasarawa.

Gwamnan yace ana tsangwamar Fulani a wasu shiyoyin Nigeria kawai Saboda suna yawon kiwata Dabbobin su, inda yace kamata yayi fulanin su hakura da tsohon tsarin kiwo irin na da Wanda shi ne yake jawowa fulanin Tsangwama a Cikin al’umma.

Yace gwamnatin jihar Kano tayi tanadi na musamman domin magance tsohon tsarin kiwon, Inda yace gwamnati ta Samar da wajen kiwo na zamani a dajin Dan soshiya domin magance Matsalolin tsaro da Kuma Kara inganta sha’anin kiwo.

Ganduje ya kalubalanci Wasu Daga Cikin fulanin wadanda suke harkokin Ta’addanci Wanda yace hakan ba dai-dai ba ne, yace kamata yayi su nemi Ilimin addini Dana zamani domin gujewa shiga harkokin da basu dace ba Cikin jahilci.

Ya yabawa Sarkin na Kano da ya Kai masa Wannan ziyara ta sada zumunci wadda ya gada Daga magabatansa ,yace Yana matukar Jin Dadin shawarwarin da Sarkin yake baiwa gwamnatin wadanda suke taimakawa wajen Kara bijiro da aiyukan da zasu ciyar da Jihar nan gaba.

Kadaura24 ta rawaito Ganduje ya baiyanawa Sarkin na Kano irin aiyukan da gwamnatinsa take yi a fannin ilimi, Lafiya, Kasuwanci, da aiyukan Raya Kasa wadanda yace Suna Kara Daga darajar jihar Kano a idanun Duniya.

Ya Kuma yabawa Mai Martaba Sarkin bisa irin Gudunmawar da suke bayarwa wajen inganta harkokin Tsaro a Kano Baki Daya, tare Kuma da ba shi tabbacin gwamnatin jihar Kano Zata cigaba da bijiro da sabbin Tsare-tsare Domin cigaban jihar Kano.

A nasa Jawabin Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya taya Gwamnan Murnar Sallah Karama tare Kuma da yadda gwamnatin take gudanar da aiyukan da suke ciyar da Kano gaba.

Sarkin yace a Matsayinsa na Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Kano Zasu cigaba da baiwa gwamnatin Kano hadin Kai da goyon bayan domin taci gaba da hidimtawa al’ummar jihar Nan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...