Ku yi addu’o’in Allah yayi Mana Maganin Yan ta’addan Kasar nan – Buhari

Date:

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya mika sakon gaisuwarsa ga Musulman kasar da ma na kasashen waje a yayin da ake shirin yin sallar Idi.

Wata sanarwa da Malam Garba Shehu, mai magana da yawun shugaban kasar ya aike wa manema labarai ranar Laraba ta ambato Shugaba Buhari yana fatan za a gudanar da bukukuwan sallah cikin “zaman lafiya, tsaro da ‘yan uwatantaka da kuma kauna ga kowa.”

Ya kara da cewa hadin kai tsakanin Musulmai da Kiristoci yana da matukar muhimmanci musamman a wannan lokaci da kasar take fama da kalubale daban-daban.

“Ya kamata mu yi addu’a tare a kan matsalolin garkuwa da mutane da hare-haren ‘yan bindiga da kuma masu neman mulkin siyasa ta hanyar shafa kashin-kaji domin ganin kasarmu ba ta ci gaba da kasance a dunkule ba,” in ji Buhari.

Shugaban kasar ya hori shugabannin siyasa da na addini da kuma masu rike da sarautun gargajiya su karfafa gwiwar ‘yan kasar wajen ganin sun kaunaci juna da kuma tausawa juna.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...