Dokar ta-baci ba za ta magance rashin tsaro a Nigeria ba – Gwamna Masari

Date:

Daga Halima M Abubakar


 Gwamna Aminu Bello Masari na jihar Katsina ya shawarci cewa sanya dokar ta baci ba zai magance kalubalen tsaro da kasar nan ke fuskanta ba.


 Masari ya ba da shawarar ne a ranar Alhamis yayin da yake amsa tambayoyin manema labaran fadar gwamnati bayan ganawarsa da Shugaban Ma’aikatan shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari, a Fadar Shugaban Kasa, Abuja.


 Idan za a iya tunawa, majalisar wakilai a ranar Talata ta nemi Shugaba Muhammadu Buhari ya gaggauta sanya dokar ta-baci a bangaren tsaro don magance matsalar rashin tsaro a kasar nan.
 A cewarsa, sojojin da za a yi amfani da su don aiwatar da irin wannan yanayin na gaggawa an riga an fadada su.


 Don haka gwamnan ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su daina sanya siyasa a cikin al’amuran tsaro, domin Sanya siyasa a sha’anin tsaro bazai haifarwa Kasar nan da Mai ido ba.


 Ya ce ba za a bar Najeriya ta wargaje ba domin hakan na nufin babbar matsala ga nahiyar Afirka baki daya.


 Masari, yayin da yake magana a kan fargabar cewa Kwamitin Raba Asusun Tarayya (FAAC) ba zai iya rarraba kason kudin na wata-wata na watan Mayu ba, ya kalubalanci hukumomin da abin ya shafa don tabbatar da hanyar da za ta kau da hakan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...